Asabar 27 Yuni 2026 - 18:53
Kallafaffen Yaƙi Na Uku Ya Fito Da Hakikanin Juyin Juya Halin Musulunci

Hauza/ Wani Malamin Hauzar Tehran ya bayyana cewa kallafaffen yaki na uku (Yakin Ramadan) ya kasance wani muhimmin lamari da ya taimaka wajen bayyana gaskiyar juyin juya halin Musulunci, ya karfafa matsayin Iran a matakin yanki da na duniya, sannan ya kawo sauyi a fagen yada labarai da gina ruwaya. Haka kuma ya jaddada muhimmancin fayyace wadannan sauye-sauye ga ra’ayin jama’a.

A cewar rahoton Kamfanin Dillancin Labaran Hauza, Hujjatul Islam wal Muslimin Hassan Ali Akbari, malamin makarantar addini ta Tehran, ya bayyana Yakin Ramadan a matsayin daya daga cikin manyan abubuwan da suka faru a tarihin juyin juya halin Musulunci, yana mai cewa wannan yaki ya haifar da sakamako masu yawa a bangarorin soja, siyasa, tattalin arziki, al’adu da kafafen yada labarai.

Ya bayyana hakan ne a wata hira da wakilin Kamfanin Dillancin Labaran Hauza a Tehran, inda ya ce daya daga cikin muhimman nasarorin wannan yaki shi ne tabbatar da gaskiyar juyin juya halin Musulunci. Ya kara da cewa abubuwan da suka faru a wannan lokaci sun nuna cewa jami’an tsarin Jamhuriyar Musulunci ta Iran suna tare da jama’a a fagen sadaukarwa da jajircewa, kuma da yawa daga cikin farfagandar karya da aka yi wa tsarin sun zama marasa tasiri.

Wannan malamin Hauza ta Tehran ya kuma yi nuni da bangaren kasa da kasa na wadannan sauye-sauye, inda ya ce tsayin dakar Iran a gaban matsin lamba da barazana ya sa matsayin kasar ya kara fitowa fili a yankin da duniya baki daya, sannan ra’ayin mutane game da Iran da ƙungiyoyin gwagwarmaya ya sauya.

Hujjatul Islam Ali Akbari ya kuma bayyana cewa daya daga cikin sakamakon wannan yaki shi ne samuwar jituwa da goyon baya daga wasu al’ummomi ga Iran, yana cewa martanin jama’a a wurare daban-daban na duniya ya nuna cewa ra’ayin jama’a ya fi mayar da hankali kan abubuwan da ke faruwa a yankin, kuma tsoffin ruwayoyi masu bangare daya sun fuskanci kalubale.

Ya ci gaba da cewa, a bangaren tattalin arziki ma, wadannan sauye-sauye sun sa wasu lissafe-lissafen tattalin arziki a yankin, musamman batun mashigar Hormuz, suka sami karin muhimmanci na dabarun siyasa da tattalin arziki, lamarin da ya kara fito da bangaren tattalin arziki na wannan rikici.

Wannan masani a harkokin addini ya kuma bayyana ci gaban da kasar ta samu a bangaren tsaro a matsayin daya daga cikin sakamakon wannan lokaci, yana cewa sabbin karfin tsaron kasar sun sauya wasu daga cikin tsoffin ma’aunin iko tare da kara karfin hana kai hari ga Iran.

Ya kuma yi nuni da rawar da kafafen yada labarai da kafofin sadarwa na zamani suka taka wajen bada labarin abubuwan da suka faru, yana cewa a wannan lokaci kafafen sada zumunta da ra’ayin jama’a sun taka muhimmiyar rawa wajen isar da hakikanin abin da ke faruwa a fili, kuma fagen yada labarai ya fita daga karkashin mallakar wani bangare kawai.

A karshe, Hujjatul Islam wal Muslimin Ali Akbari ya jaddada muhimmancin rawar da malaman Hauza da jami’o’i za su taka wajen fayyace wadannan sauye-sauye, yana mai cewa a yau fiye da kowane lokaci ya zama dole a gabatar da sahihin hoto kuma bayyananne game da gaskiyar Iran da sauye-sauyen yankin ga jama’ar cikin gida da na duniya.

Alamomi

Ra'ayinka

You are replying to: .
captcha